No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta bayyana cewa, rundunar ta ɗauki matakin daƙile wasu ‘yan bindiga guda biyu tare da daƙile wani hari da aka kai wa wasu al’umma a ƙaramar hukumar Tsafe.

Wata sanarwa a ranar Litinin a Gusau ta hannun Kakakin Rundunar, CSP Muhammad Shehu, ya ce Kwamishinan ‘yan sandan, Kolo Yusuf ya yaba da jajircewar ‘yan sandan.

Ya kuma tabbatar wa mazauna yankin cewa rundunar ta himmatu sosai wajen daƙile sake bullar miyagun laifuka a faɗin jihar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan Sanda sun kama ɗan gidan yarin Kuje da ya gudu

“An fatattaki ‘yan bindigar da suka yi yunƙurin kai wa al’umma hari, inda aka kashe biyu daga cikin waɗanda ake zargin ‘yan bindigar ne, yayin da wasu suka gudu da raunukan harbin bindiga.

“Kwamishanan ‘yan sandan ya kuma yaba da ƙoƙarin haɗin gwiwa da ‘yan sanda da sojoji ke yi a jihar, domin daƙile matsalar ‘yan fashi da makami da sauran miyagun laifuka,” in ji shi.

Shehu ya yi ƙira ga jama’a da su ci gaba da baiwa jami’an tsaro goyon baya a ƙoƙarin da suke na maido da dawwamammen zaman lafiya da tsaro a jihar.

Ya ce rundunar za ta ci gaba da inganta tare da ɗorewar yaƙi da ‘yan bindiga a jihar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...