No menu items!

Sample Page Title

Date:

An sako Farfesa Onje Gye-Wado, tsohon mataimakin gwamnan jihar Nasarawa da wasu ‘yan bindiga suka sace ranar 7 ga watan Afrilu.

DSP Ramhan Nansel, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, PPRO, ne ya tabbatar da hakan ga Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya a ranar Litinin a Lafiya.

Kun tuna cewa Gye-Wado wanda ya kasance mataimakin gwamna tsakanin 1999 zuwa 2003 a gwamnatin Abdullahi Adamu, an yi garkuwa da shi a gidansa da ke ƙaramar hukumar Wamba.

KU KUMA KARANTA: Yadda ‘yan sanda suka ceto ɗan jarida daga hannun masu garkuwa da mutane

PPRO ya ce tsohon mataimakin gwamnan ya sami ‘yanci ne da misalin ƙarfe 9:00 na daren Lahadi, kuma tuni ya koma cikin iyalansa.

Nansel wanda ya ce har yanzu ba a kama su ba, ya ƙara da cewa ‘yan sandan ba su da masaniyar wani kuɗin fansa da aka biya kafin a sako su.

A cewarsa, an saki dattijon ne saboda ci gaba da matsin lamba da haɗin gwiwar jami’an tsaro suka yi wa masu garkuwar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...