No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta bayyana ranar da za a sake gudanar da zaɓukan jihohin Kebbi da Adamawa.

Mista Rotimi Lawrence Oyekanmi, babban sakataren yaɗa labarai na shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana hakan a Abuja, a ranar Litinin.

Ya ce za a gudanar da zaɓukan gwamnoni da na ‘yan majalisun tarayya da na jihohi a rana guda.

“Hakan ya taso ne daga taron da ta gudanar a yau, INEC ta yanke shawarar cewa za a gudanar da dukkan zaɓukan gwamnoni da na ‘yan majalisun tarayya da na jihohi a ranar Asabar 15 ga Afrilu, 2023,” in ji Oyekanmi.

KU KUMA KARANTA: Anyi inkwankulusib a zaɓen Adamawa

Ya ce nan ba da jimawa ba za a fitar da cikakken bayani a hukumance.

Zaɓukan shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun tarayya da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu da kuma na gwamnoni da na majalisun jihohi na ranar 18 ga Maris sun shaida soke zaɓen da wasu zaɓukan da ba a kammala ba a faɗin kasar nan ba, waɗanda sune INEC ta bada sanarwar za ayi su a watan gobe.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...