No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta tarwatsa sansanin ‘yan bindiga tare da ceto mutane 14 da aka yi garkuwa da su a Zamfara.

Waɗanda abin ya shafa dai sun shafe kwanaki 68 a hannun masu garkuwa kafin daga bisani ‘yan sanda su kubutar da su.

A cewar rahoton da kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN), ya fitar a cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Muhammad Shehu ya fitar ranar Asabar a Gusau.

A cewarsa, “A ranar 10 ga Maris, 2023, jami’an ‘yan sanda tare da ’yan banga, yayin da suke aikin sintiri a kusa da dajin Munhaye, sun yi nasarar fatattakar wasu sansanin ‘yan bindiga mallakar wani sarkin ‘yan fashi da makami, wanda aka fi sani da Dogo Sule.

“Sakamakon aikin, an kubutar da mutane 14 da aka yi garkuwa da su, waɗanda suka hada da manya maza biyu, mata bakwai da yara biyar ‘yan ƙasa da shekara biyu.

KU KUMA KARANTA: Yadda ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da mutane 53, suka kashe mata masu juna biyu a wasu ƙauyuka huɗu a Neja

“Waɗanda abin ya shafa sun sanar da jami’an ‘yan sanda cewa, a ranar 1 ga watan Janairun 2023, da misalin ƙarfe 11 na dare , wasu da dama da ake zargin ‘yan bindiga ne ɗauke da manyan makamai, suka afkawa ƙauyukan Anguwar Mangoro da Gidan Maidawa a ƙaramar hukumar Gusau, suka yi awon gaba da wadanda abin ya shafa zuwa sansaninsu, inda suka shafe kwanaki 68 a tsare.

“Waɗanda lamarin ya rutsa da su suna cikin mawuyacin hali, kuma an kai su asibitin ‘yan sanda da ke Gusau domin kula da lafiyarsu, daga nan kuma aka haɗasu da ‘yan uwansu,” in ji Shehu.

Ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mista Kolo Yusuf, ya taya waɗanda abin ya shafa murna domin samun ‘yancinsu, ya kuma ba da tabbacin ci gaba da jajircewar rundunar na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan ƙasa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

3 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...