No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wasu masu kaɗa kuri’a a Ozubulu da ke ƙaramar hukumar Ekwusigo a Anambra, sun ba da kansu a matsayin jami’an wucin gadi na hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa, INEC, bayan da waɗanda aka aiko suka kasa fitowa aikin zaɓen.

Masu aikin sa kai sun maye gurbin ma’aikatan wucin gadin ne domin tabbatar da cewa an gudanar da zaɓe a rumfunan zaɓe 006, 007, da 008 a makarantar Uruokwe Central School da ke Ozubulu, ƙaramar hukumar Ekwusigo a ranar Asabar.

Rahotanni sun nuna cewa tun da farko wasu mambobin ƙungiyar da suka samu horo tare da tura su aikin zaɓe a rumfunan zaɓe ba su bayyana ba a ranar Asabar.

Sai dai shuwagabannin da ba ‘yan INEC ba ne suka bayar da rahoton yin aiki inda wasu masu kaɗa kuri’a suka ba da kansu don yin aiki a matsayin jami’an wucin gadi.

KU KUMA KARANTA: Kuɗi shine mabuɗin shirye-shiryen gudanar da aiki a ranar zaɓe – Jega

Hakan, ya haifar da ƙalubale yayin da masu aikin sa kai ba su da horo kuma suna da matsala wajen tafiyar da tsarin tantance masu kaɗa kuri’a (BVAS) da kuma bin tsarin da aka gindaya na atisayen.

Haka lamarin ya kasance a rumfunan zabe 018 da 019, a dakin taro na Umuanyiegbu, Ward 004, Ozubulu, Ekwusigo LGA. Shugabannin sun ƙi yin magana da ‘yan jarida da kuma ƙoƙarin ganin kwamishiniyar zaɓe ta INEC, Dr. Elizabeth Agwu, don ta bada bayani yaci tura.

Har ila yau a Enugu, an ga wasu masu aikin sa kai musamman matasa suna taimakawa wasu ma’aikatan wucin gadi wajen kafa rumfunan zaɓe da kuma tabbatar da tsaro a wasu yankunan jihar.

A Kwalejin Gwamnatin Tarayya da ke Enugu, ɗaya daga cikin ‘yan agajin da aka fi sani da Nonso, ya bayyana cewa ya yanke shawarar taimakawa ne domin ganin an gudanar da zaben cikin sauki. “Na yanke shawarar taimaka don shawo kan ɗimbin jama’a.

Tun bayan gudanar da babban zaɓe a kasar nan ban taba ganin irin wannan fitowar jama’a ba. “Don haka, ni da abokaina mun sadaukar da kai don taimakawa tunda akwai jami’an tsaro kaɗan a rumfar zaɓe,” inji shi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...