No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tsohon shugaban jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya wato tsohon VC na ABU da shugaban sashen kuɗi na jami’ar wato Bursar, Farfesa Ibrahim Garba, da Ibrahim Shehu Usman sun gurfanar a gaban mai shari’a A.A Bello na babbar kotun jihar Kaduna bisa tuhume-tuhume takwas da suka hada da sata da kuma karkatar da kuɗaɗe sama da Naira biliyan ɗaya.

Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon kasa, (EFCC) ce ta jagoranci gurfanar da waɗabda ake zargi.

KU KUMA KARANTA:EFCC ta sake gurfanar da tsohon gwamnan Kaduna a kotu

Shari’ar dai ya biyo bayan bincike na tsanaki na tsawon watanni da wata kotu ta shigar inda ake zargin mutanen biyu da karkatar da kuɗaɗen da aka tanada don gyaran zauren taro na Kongo a Zariya.

Binciken ya tabbatar da cewa wadanda ake tuhumar sun sace sama da Naira biliyan ɗaya daga asusun ajiyar ma’ikatar tare da karkatar da su zuwa asusu na ƙashin kansu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...