No menu items!

Sample Page Title

Date:

Dogayen layuka a gidajen mai na daga cikin alamun da ‘yan Najeriya ke la’akkari da su wajen yiwuwar samun karancin man fetur a kasar.WASHINGTON D.C. — 

Kamfanin man fetur na Najeriya NNPC ya ba da tabbacin cewa kasar na da wadataccen mai a ajiye wanda zai iya biyan bukatun daukacin ‘yan Najeriya.

NNPC ya fitar da wannan sanarwa ce a ranar Laraba bayan da layukan mai suka fara kunno kai a Abuja, babban birnin kasar.

Sai dai cikin sanarwar mai dauke da sa hannun Babban Manajan yada labaran kamfanin Garbadeen Muhammad, NNPC ya yi kira ga jama’a da su kwantar da hankulansu.

“Kamfanin NNPC na mai sanar da ku cewa yana da wadataccen mai a ajiye wanda zai biya bukatun ‘yan Najeriya.

“Muna kira ga jama’a da kada su yi ta tururuwar sayen man, su yi watsi da jita-jitar da ke nuna cewa za a samu karancin man.” Garbadeen Muhammad ya ce.

‘Yan Najeriya dai kan yi rige-rigen sayen man fetur su ajiye, a wani mataki na kandagarki, idan sun ga alamu da ke nuna cewa za a samu karancin man.

Dogayen layuka a gidajen mai na daga cikin alamun da ‘yan Najeriya ke la’akkari da su wajen yiwuwar samun karancin man fetur a kasar.

admin
adminhttps://neptuneprimehausa.com
Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...