No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ɗangote ya sake rage farashin litar man fetur

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Kamfanin matatar Ɗangote  ya rage farashin man fetur  zuwa ₦899.50k a kowace lita.

Wannan sanarwa ta fito ne cikin wata takarda da aka fitar da safiyar Alhamis.

Kamfanin ya bayyana cewa an ɗauki wannan matakin ne domin “bada sauƙi ga ‘yan Najeriya kafin lokacin bukukuwan ƙarshen shekara.”

KU KUMA KARANTA: Matatar mai na Ɗangote ya rage farashin fetur ɗinsa

Matatar mai ta farko mai zaman kanta a nahiyar Afrika, wadda a baya ta rage farashin zuwa ₦970 a kowace lita a ranar 24 ga watan Nuwamba, yanzu ta sanar da sabon farashi na ₦899.50k a kowace lita.

“Wannan ragin farashin an yi shi ne da nufin rage kudin sufuri a lokacin bukukuwan karshen shekara,” in ji sanarwar da Babban Jami’in Yaɗa Labarai na Kamfanin, Anthony Chiejina, ya sa hannu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...