Connect with us

Labarai

Ɗan fari ya kashe ɗan autansu da duka, ya raba kansa gida biyu

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta kama wani matashi ɗan shekara 24 mai suna Amos Christopher bisa zarginsa da lakaɗa wa ƙaninsa duka ya mutu har Lahira.

Wanda ake zargin wanda aka ce yana fama da ciwon farfaɗiya, ana zargin ya kashe ɗan su na ƙarshe, Thyson Christopher mai shekaru 4, daga bisani kuma ya fille kansa a ranar Litinin, 19 ga watan Yuni.

A cewar rundunar ‘yan sandan, wanda ake zargin wanda shi ne na farko a gidansu, ya yanke jiki ya faɗi a ranar 18 ga watan Yuni, inda maƙwabta suka ɗauko shi suka dawo da shi gida.  

An ba da rahoton cewa yanayin lafiyarsa ya taɓarɓare tare da sauya halayensa da safe ya far wa mahaifiyarsa da ƙannensa da ke gida tare da shi da ƙarfi. 

KU KUMA KARANTA: Wasu ‘yan bindiga sun kashe ma’aikacin INEC, sun sace matarsa a Ebonyi

An ruwaito cewa ya kama yaron ɗan shekara 4 ya ja shi zuwa cikin ɗaki inda ya kulle kofar ya yi masa duka ya mutu har Lahira.  

Duk ƙoƙarin ceto yaron da mahaifiyarsa ta yi ya ci tura.  A halin da yake ciki na tashin hankali, an yi zargin ya kai gawar waje inda ya yi amfani da fartanya da ke hannunsa wajen datse kan yaron tare da fasa kan gida biyu.

A yayin da Kakakin Rundunar SP Suleiman Yahaya Nguroje ke yi masa tambayoyi, wanda ake zargin da ƙyar ya yi magana ya ce bai yi komai ba, kuma ƙanin nasa yana gida.

Da yake amsa tambayoyi, mahaifin waɗanda ake zargi da kuma wanda aka kashe, Christopher Haruna, ya ce lamarin ya faru ne a lokacin da yake gona, ya kuma tabbatar da cewa Amos na fama da farfaɗiya.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Wani mutum ya lakaɗa wa budurwarsa duka ta mutu har lahira a Kuros Riba | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like