No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ɗalibai Sun nemi a soke sakamakon Jarabawar JAMB baki ɗaya

Daga Shafaatu Dauda Kano

Wasu daga cikin daliban da suka zana jarabawar neman gurbi a makarantun gaba da sakandire JAMB, sun nemi a soke sakamakon jarrabawar na wannan shekara baki ɗaya, biyo bayan amincewar da hukumar JAMB tayi na cewa an samu kuskure yayin jarrabawar, kuma itace da alhakin kuskuren.

Daliban sun shaidawa Daily trust, cewa an samu gagarumin rashin nasara a JAMB, biyo bayan matsalolin da aka fuskanta, kuma hukumar JAMB itace ke da alhakin haddasa wannan matsala.

KU KUMA KARANTA: Shugaban ƙaramar hukumar Katagum ya raba wa al’umma tallafin kayan masarufi

Dalibai fiye da miliyan daya da rabi ne suka gaza samun maki da yakai 200, kuma hakan zai iya sanyawa mafi yawa daga ɗalibai su rasa damar shiga jami’a a wannan lokaci.

Wasu daliban sunce an samu matsaloli a cibiyoyin rubuta jarrabawar, sannan a wasu guraren ba’a bawa dalibai isasshen lokaci ba, wanda ake alaƙanta hakan da taimakawa ta fuskar faɗuwar daliban da aka samu.

A jiya Laraba, ne shugaban hukumar JAMB Farfesa Ishaq Oloyede, ya fashe da kuka yayin zantawar sa da manema labarai, inda ya tabbatar da cewa sune da alhakin rashin nasarar ɗalibai a jarrabawar, sannan ya nemi ayi musu afuwa.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...