No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ƴan sandan Isra’ila sun kama mutum bakwai daga cikin masu zanga-zanga saboda yin tarzoma a kusa da Titin Begin don neman a kuɓutar da mutanen da aka yi garkuwa da su a Gaza.

“Jam’ain ƴan sandan Isra’ila sun kama mutum 7 a Dandalin Kaplan da ke birnin Tel Aviv bisa zarginsu da yin tarzoma a yayin zanga-zangar da ke neman gwamnati ta sasanta da ƙungiar Hamas domin ta saki mutanen da ta yi garkuwa da su a Gaza,” in ji jaridar Yedioth Ahronoth.

Ta ƙara da cewa wasu masu zanga-zanga sun toshe hanyar da ake kira Begin Street — wata hanya mai matuƙar muhimmanci a Tel Aviv — a wani ɓangare na ƙoƙarin matsa lamba kan gwamnati don ta ɗauki mataki.​​​​​

A Yammacin Birnin Ƙudus, ɗaruruwan ƴan Isra’ila sun yi zanga-zanga a kusa da gidan Firaiminista Benjamin Netanyahu, inda suka buƙaci ya yi sulhu da ƙungiyar Falasɗinawa ta Hamas.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe mata da yara sama da 25,000 a Gaza — Pentagon

Kazalika masu zanga-zangar sun yi kira a gudanar da zaɓe ba tare da ɓata lokaci ba, a cewar Yedioth Ahronoth.

A yankin Caesarea da ke arewacin Isra’ila, mutum kimanin 1,200 sun yi zanga-zanga a kusa da gidan Netanyahu, inda suka buƙaci a saki mutanen da aka yi garkuwa da su sannan ya sauka daga mulki, kamar yadda kafar watsa labaran gwamnatin Isra’ila ta rawaito.

Masu zanga-zangar sun riƙa yin ihu suna sukar gwamnatin Netanyahu inda suka dinga maimaita cewa, “A gudanar da zaɓe nan-take!”

Haka kuma dubban Isra’ilawa sun yi zanga-zanga a wasu yankuna na ƙasar, ciki har da Haifa, Raanana da Rehovot.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...