Connect with us

Laifi

Ƴan sanda a jihar Yobe sun kama wata mata da kashe mijinta da wuƙa

Published

on

Abin da ya sa aka ba da belin matar da ake zargi da kashe mijinta a Damaturu - Suleiman Hassan Gimba Esq

Ƴan sanda a jihar Yobe sun kama wata mata da kashe mijinta da wuƙa

Ana zargin wata matar aure, Zainab Isa, mai kimanin shekara 22 ta kashe mijinta Ibrahim Yahaya Mai kimanin shekara 25 mazaunin unguwar Abbati cikin garin Damaturu a Jihar Yobe.

Lamarin ya faru ne sakamakon taƙaddamar da ta auku tsakanin ma’uaratan ranar Talata wadda ya kai ga ta soka wa mijinta nata wuƙa kuma nan take ya ce ga garinku nan.

Wata majiyar da ke unguwar ta Abbari ta bayyana cewar, ma’auratan sun daɗe suna takun saƙa a tsakaninsu, amma abinka da ajali taƙaddamar ƙarshen ita ce ta kai ga matar ta aika da mijin nata lahira.

Rundunar ’yan sandan Jihar Yobe ta bakin kakakinta, DSP Dungus Abdulkarim ta tabbatar da faruwar wannan mummunan lamari.

Wakilinmu ya ruwaito cewa DSP Dungus ya yi wa manema labarai ƙarin haske kan faruwar lamarin da misalin ƙarfe 10 na safiyar ranar 26 ga Yuni a hedikwatar ’yan sanda ta C Division a da ke birnin Damaturu.

Kakakin ’yan sandan ya ce sun samu ƙorafin faruwar lamarin daga wani maƙwabcin ma’auratan da ke unguwar ta Abbari.

Ya ce makwabcin ya bayyana musu cewar ma’auratan sun yi musayar yawu a tsakaninsu, lamarin da ya rikiɗe zuwa rikici.

KU KUMA KARANTA: An kama wani matashi ɗan shekara 25 da laifin kashe mahaifinsa da wuƙa a Kano (Bidiyo)

Bayanai sun ce ana tsakar jayayyar ce sai matar ta yi amfani da wuƙa ta daɓa wa mijin a ƙirji, kuma daga baya ya mutu sakamakon mummunan rauni da ya samu kafin tawagar ‘yan sanda ta ƙaraso gidan.

DSP Dungus tuni aka miƙa matar sashen binciken manyan laifuffuka domin ɗaukar matakan da suka dace gabanin gurfanar da uta a gaban kuliya.

A bayanin da ta yi wa ’yan sandan, matar ta ce ba ta yi niyyar kashe mijinta ba, sai dai ta daɓa masa wuƙa ne domin ta kare kanta sakamakon dukan tsiya yake mata a lokacin faruwar lamarin duk da cewa ba ta gama samun sauƙi daga tiyatar da aka yi mata kwanan nan a dalilin haihuwar da ta yi ƙasa da wata guda.

Ta ci gaba da cewa “mun sha fuskantar matsaloli da tashin hankali a rayuwar aurenmu.

“Kusan kullum sai mun yi rikici da shi [mijin nawa] musamman idan na nemi kuɗin cefanen abinci tun lokacin aurenmu har bayan haihuwar ɗanmu na farko da na biyu.”

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Garba Ahmed, ya buƙaci ma’aurata da su riƙa miƙa rahoton  duk wani nau’i na cin zarafinsu da suke fuskanta a tsakaninsu ga mahukunta mafi kusa.

Kwamishinan ya ce wannan ita kaɗai ce hanyar da za a samu mafita mai ɗorewa ko kuma a kai ƙara kotu ko kuma miƙa wa ’yan uwa mafi kusa ƙorafi domin a yi musu sulhu maimakon ɗaukar mummunan mataki irin haka.

Ya kuma yi ƙira da umartan ’yan uwa da su riƙa  magance matsalolin da suka shafi zamantakewar aure kan lokaci don hana ta’azzara daga ƙananan rikice-rikice zuwa manya kamar kisan kai.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda

Published

on

Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda

Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda

Daga Ibraheem El-Tafseer

Aƙalla mutane shida ne suka mutu inda wasu 15 suka jikkata a wani harin ƙunar baƙin wake da aka kai a garin Gwoza na jihar Borno.

Wani abin takaici ya faru ne a lokacin da ‘yar ƙunar baƙin wake ta tayar da bam a garin Gwoza, ranar Asabar.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, (NAN), ya ruwaito cewa an kai harin ne a wani wurin shaƙatawa na motoci da ake ƙira Marrarraban Gwoza.

Kwamishinan ‘yansandan jihar Borno Yusuf Lawal ya tabbatar da faruwar harin yana mai cewa wata ‘yar ƙunar baƙin wake ce ta kai harin.

Lawal ya ce jami’in ‘yansandan shiyyar Gwoza ne ya sanar da shi cewa aƙalla mutane shida ne suka mutu inda aka kwashe wasu 15 zuwa asibiti.

Wani ganau mai suna Buba, ya shaida wa NAN cewa ‘yar ƙunar baƙin waken ta nufi tsakiyar wani bikin aure ne, inda ta tayar da bam ɗin a nan.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Buba ya ce harin ya rusa farin ciki da murnar wannan rana ta musamman, inda ya bar iyalai da ‘yan uwa cikin makoki.

Wani wanda ya shaida lamarin, Muhammed Kasim, ya ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 1:30 na rana.

“Mun ji ƙarar fashewar abubuwa, tare da ƙura, sai muka ga gawarwaki a ƙasa.”

Ya ce an kwashe da dama daga cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su zuwa asibiti yayin da aka tura jami’an tsaro domin dawo da zaman lafiya a yankin. (NAN).

Continue Reading

Laifi

’Yan sanda sun kama wani matashi kan zargin satar kuɗi ta na’urar ATM

Published

on

’Yan sanda sun kama wani matashi kan zargin satar kuɗi ta na’urar ATM

’Yan sanda sun kama wani matashi kan zargin satar kuɗi ta na’urar ATM

Daga Muhammad Kukuri

Rundunar ’yan sandan jihar Gombe ta kama matashin, wanda ake wa inkiya da Mai Shanawa ne kan zargin aikata yaudara da satar kuɗi da katin ATM ta na’urar PoS.

Matashin ya faɗa komar ’yan sanda ne bayan wani mazaunin garin Abuja Bula, da ke Karamar Hukumar Kwami ya kai rahoto ofishin ’yan sanda na Dukku a ranar 22 ga Watan Mayu 2024.

Muhammad yana zargin matsahin da yaudarar sa da kuma satar kudi a asusun bankinsa a banki a lokacin da yaje cire kuɗi da katinsa na ATM.

Ya ce bayan ya saka katinsa  na’urar ATM ba ta ba shi kudin ba, ashe matashin yana biye da shi a baya, sai ya yaudare shi cewa ya shiga cikin banki ya yi musu bayani.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sandan Najeriya sun kama waɗanda ake zargi da satar mutane a titin Abuja-Kaduna

Bai ankara ba, ashe a lokacin matashin ya zare masa katin ya bar shi a wajen.

Mutumin ya ci gaba da cewa, yana tsaye yana jira can sai yaga sako an cire Naira dubu ɗari uku daga asusunsa ta wani POS da ke kusa da bankin a garin na Dukku.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, ASP Buhari Abdullahi, ya ce bayan  samun rahoton ƙorafin suka shiga bincike suka yi sa’ar kama wanda ake zargin.

ASP Buhari Abdullahi ya ce a yayin binciken sun samu katunan cire kuɗi na ATM daban-daban har guda 21, ciki harda na wanda ya kai ƙorafin, a hannun matashin.

Sannan ya ce suna kan ci gaba da bincike, da zarar sun kammala za su tura wanda ake zargin zuwa kotu.

Continue Reading

Laifi

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Published

on

'Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaki Rarara

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Daga Idris Umar, Zariya

Labarin dake zuwa mana yanzu shine ’yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar shahararren mawaƙin siyasa, Dauda Kahutu Rarara.

Kamar yadda akace an yi garkuwa da Hajiya Hakima Adamu ne a gidanta da yankin Kahutu a ƙaramar hukumar Ɗanja ta jihar Katsina, kamar yadda aka tseguntawa manema labarai

Wasu mutane a ƙauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi gaba da ita.

“A kafa suka zo, kuma kasancewar ba su yi harbi ba a lokacin da suka kai harin suka yi garkuwa da ita cikin ’yan mitoci. Dattijuwar ba ta yi musu turjiya ba a lokacin da suka ce ta biyo su.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai da dama a jihar Delta

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka suka tafi da ita.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda suna dauke da bindigogi,” in ji wani mazaunin kauyen na Kahutu, kamar yadda majiyarmu ta jiyo.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like