Laifi
Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 a Kaduna, sun kai hari a ofishin ƴan sanda a Zamfara
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/02/Screenshot_20240219-091157_1.jpg)
Wasu ƴan bindiga sun kai hari a ƙaramar hukumar Kajuru da ke Kaduna a arewacin Najeriya ranar Lahadi inda suka ƙona aƙalla mutum 12 da ransu, a cewar mazauna yankin.
Harin, wanda ƴan bindigar suka kai a ƙauyen Gindin Dutse Makyali, ya yi sanadin jikkatar mutum 15 bayan an cinna wa gidajensu wuta, in ji Isa Yusuf, wani shugaban matasan yankin a hira ta wayar tarho da kamfani dillancin labarai na Anadolu.
“Sun yi ta buɗe wuta, abin da ya sa muka ji tsoron fita daga gidajenmu. Don haka, sai suka cinna wuta a gidajen mutane inda suka kashe mutum 12 a cikin gidajensu, kana mutum kusan 15 suka ji munanan raunuka,” a cewarsa.
KU KUMA KARANTA: Sojojin Najeriya sun kashe ƴan ta’adda 254 a cikin mako guda
Isa Yusuf ya ƙara da cewa ƴan bindigar sun ƙone gidaje 17, yana mai cewa an kai mutum 15 da suka ji raunuka asibitin da ke kusa domin kula da su.
Mai magana da yawun ƴan sandan Kaduna Mansur Hassan ya tabbatar wa Anadolu aukuwar lamarin, yana mai cewa an tura ƙarin ƴan sanda na musamman yankin domin “hana kai ƙarin hare-hare da kuma kwantar da hankulan mazauna yankin.”
A jihar Zamfara, hukumomi sun tabbatar da cewa wasu ƴan bindiga sun kai hari wasu wurare a ƙaramar hukumar Zurmi ciki har da ofishin ƴan sanda ranar Lahadi.
Ganau sun ce ƴan bindigar sun kai hari a garin ne da maraice inda suka kashe mutum bakwai har da wani ɗan sanda.
Sun ƙara da cewa ƴan bindigar sun je garin ne domin yin ramuwa bisa kisan wasu abokansu biyu da ƴan banga suka yi.
Kafofin watsa labaran Najeriya sun ambato kakakin rundunar ƴan sandan Zamfara Yazid Abubakar yana tabbatar da kai harin, ko da yake bai yi ƙarin bayani ba.
Labarai
Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda
![Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/06/IMG-20240629-WA0099.jpg)
Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda
Daga Ibraheem El-Tafseer
Aƙalla mutane shida ne suka mutu inda wasu 15 suka jikkata a wani harin ƙunar baƙin wake da aka kai a garin Gwoza na jihar Borno.
Wani abin takaici ya faru ne a lokacin da ‘yar ƙunar baƙin wake ta tayar da bam a garin Gwoza, ranar Asabar.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, (NAN), ya ruwaito cewa an kai harin ne a wani wurin shaƙatawa na motoci da ake ƙira Marrarraban Gwoza.
Kwamishinan ‘yansandan jihar Borno Yusuf Lawal ya tabbatar da faruwar harin yana mai cewa wata ‘yar ƙunar baƙin wake ce ta kai harin.
Lawal ya ce jami’in ‘yansandan shiyyar Gwoza ne ya sanar da shi cewa aƙalla mutane shida ne suka mutu inda aka kwashe wasu 15 zuwa asibiti.
Wani ganau mai suna Buba, ya shaida wa NAN cewa ‘yar ƙunar baƙin waken ta nufi tsakiyar wani bikin aure ne, inda ta tayar da bam ɗin a nan.
KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara
Buba ya ce harin ya rusa farin ciki da murnar wannan rana ta musamman, inda ya bar iyalai da ‘yan uwa cikin makoki.
Wani wanda ya shaida lamarin, Muhammed Kasim, ya ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 1:30 na rana.
“Mun ji ƙarar fashewar abubuwa, tare da ƙura, sai muka ga gawarwaki a ƙasa.”
Ya ce an kwashe da dama daga cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su zuwa asibiti yayin da aka tura jami’an tsaro domin dawo da zaman lafiya a yankin. (NAN).
Laifi
’Yan sanda sun kama wani matashi kan zargin satar kuɗi ta na’urar ATM
![’Yan sanda sun kama wani matashi kan zargin satar kuɗi ta na’urar ATM](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/06/IMG-20240628-WA0175.jpg)
’Yan sanda sun kama wani matashi kan zargin satar kuɗi ta na’urar ATM
Daga Muhammad Kukuri
Rundunar ’yan sandan jihar Gombe ta kama matashin, wanda ake wa inkiya da Mai Shanawa ne kan zargin aikata yaudara da satar kuɗi da katin ATM ta na’urar PoS.
Matashin ya faɗa komar ’yan sanda ne bayan wani mazaunin garin Abuja Bula, da ke Karamar Hukumar Kwami ya kai rahoto ofishin ’yan sanda na Dukku a ranar 22 ga Watan Mayu 2024.
Muhammad yana zargin matsahin da yaudarar sa da kuma satar kudi a asusun bankinsa a banki a lokacin da yaje cire kuɗi da katinsa na ATM.
Ya ce bayan ya saka katinsa na’urar ATM ba ta ba shi kudin ba, ashe matashin yana biye da shi a baya, sai ya yaudare shi cewa ya shiga cikin banki ya yi musu bayani.
KU KUMA KARANTA: Ƴan sandan Najeriya sun kama waɗanda ake zargi da satar mutane a titin Abuja-Kaduna
Bai ankara ba, ashe a lokacin matashin ya zare masa katin ya bar shi a wajen.
Mutumin ya ci gaba da cewa, yana tsaye yana jira can sai yaga sako an cire Naira dubu ɗari uku daga asusunsa ta wani POS da ke kusa da bankin a garin na Dukku.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, ASP Buhari Abdullahi, ya ce bayan samun rahoton ƙorafin suka shiga bincike suka yi sa’ar kama wanda ake zargin.
ASP Buhari Abdullahi ya ce a yayin binciken sun samu katunan cire kuɗi na ATM daban-daban har guda 21, ciki harda na wanda ya kai ƙorafin, a hannun matashin.
Sannan ya ce suna kan ci gaba da bincike, da zarar sun kammala za su tura wanda ake zargin zuwa kotu.
Laifi
‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara
!['Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaki Rarara](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/06/IMG-20240628-WA0173.jpg)
‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara
Daga Idris Umar, Zariya
Labarin dake zuwa mana yanzu shine ’yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar shahararren mawaƙin siyasa, Dauda Kahutu Rarara.
Kamar yadda akace an yi garkuwa da Hajiya Hakima Adamu ne a gidanta da yankin Kahutu a ƙaramar hukumar Ɗanja ta jihar Katsina, kamar yadda aka tseguntawa manema labarai
Wasu mutane a ƙauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi gaba da ita.
“A kafa suka zo, kuma kasancewar ba su yi harbi ba a lokacin da suka kai harin suka yi garkuwa da ita cikin ’yan mitoci. Dattijuwar ba ta yi musu turjiya ba a lokacin da suka ce ta biyo su.
KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai da dama a jihar Delta
“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka suka tafi da ita.
“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda suna dauke da bindigogi,” in ji wani mazaunin kauyen na Kahutu, kamar yadda majiyarmu ta jiyo.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano
Pingback: ’Yan acaɓa sun kai hari ofishin ’yan sanda a Legas