Connect with us

NLC

Ƙungiyar NLC ta gudanar da zanga-zanga, saboda tsadar rayuwa a faɗin Najeriya

Published

on

Mambobin Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya wato (NLC) sun gudanar da zanga-zanga a faɗin ƙasar sakamakon matsin rayuwa, yunwa da taɓarɓarewar tattalin arziƙi a ƙasar.

Zangar-zangar na zuwa ne biyo bayan da ƙungiyar ƙwadago da gwamnatin tarayyar ƙasar suka gana a jiya Litinin, a wani mataki na kawo tsayar da zanga-zangar, amma taron ya ƙare ba tare da an cimma matsaya ba tsakanin ɓangarorin biyu.

Tun da misalin ƙarfe 7 na safe ne mambobin ƙungiyar ta NLC suka fara taruwa a sassa daban-daban na Najeriya, ɗauke da kawalaye mai ɗauke da mabambantan saƙonni da kuma sanya tufaffi mai tambarin ƙungiyar NLC.

Saƙonnin mabambanta dake kan kwalayen da mambobin ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya suka riƙe sun haɗa da ”a kawo ƙarshen yunwa da matsin tattalin arziƙi a ƙasar”, ”gwamnati ta sake salo wajen sauraron koken al’umma ganin yadda talaka baya iya samun abinci”, “a yau ana sayar da buredi a kan naira 150”.

A birnin tarayya Abuja, mambobin ƙungiyar NLC sun taru a harabar hedikwatar ƙungiyar dake unguwar Central Area sannan suka fara tattakin zangar-zangar daga nan har zuwa majalisun tarayyar Ƙasar.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ayyana yajin aikin gargaɗi na kwana biyu kan cire tallafin mai

Mambobin ƙungiyar NLC sun taru a harabar hedikwatar ƙungiyar dake unguwar Central Area.

A jihar Neja dake maƙwabtaka da birnin tarayya Abuja, shugaban ƙungiyar ƙwadago ta NLC a jihar ne ya jagoranci mambobinta zuwa harabar majalisar dokokin jihar sakamakon halin matsin rayuwa da ‘yan ƙasa ke ciki da kuma yadda mambobin ƙungiyar ke ci gaba da kokawa kan mummunar tasirin da hare-haren ‘yan bindiga da sauran miyagu ke yi ga matsalar yunwa da ake ciki.

A wani ɓangare kuma wasu ‘yan Najeriya ƙarƙashin ƙungiyar kare haƙƙin fararen hula wato Network of Civil Society for Accountability sun fito zanga-zangar nuna goyon baya ga shugaba Bola Tinubu inda suka riƙe takarda mai mabambantan saƙonni kamar “dole ne mu yi haƙuri da Shugaban Ƙasa, mu ba shi lokaci don kawo sauyin da ake buƙata.

Ƙungiyar NLC dai na zanga-zangar nuna halin matsin da ake ciki a ƙasar na yini biyu don farkar da gwamnati a kan nauyin da ya rataya a wuyanta.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

NLC

Ƙungiyar ƙwadago ta buƙaci gwamnati ta biya ma’aikata 615,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Published

on

Ƙungiyar Ƙwadago ta ƙasa ta NLC tare da TUC ta ‘yan kasuwa, sun nemi gwamnati ta biya 615,000 ga ko wane ma’aikaci a matsayin mafi ƙarancin albashi, sai dai wasu na ganin abu ne mai wuya idan an yi la’akari da zunzurutun bashin da ake bin Najeriya, wasu kuma suna ganin yaudara ce kawai.

Ƙungiyoyin sun tabbatar da cewa sun aike wa kwamitin da mataimakin Shugaban ƙasa ya naɗa domin duba yadda za a inganta albashin ma’aikata ba tare da tayar da jijiyoyin wuya ba.

Kwamred Nasir Kabir, shugaban tsare-tsare na ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa, ya ce mafi ƙarancin albashin (₦615,000) shi ne abin da suka amince da shi, kuma a kansa za su tsaya, babu gudu babu ja da baya.

Nasir ya ce inda a ra’ayinsa ne, abin da ya kamata a biya ko wanne ma’aikaci ya zama aƙalla Naira miliyan ɗaya duk wata.

KU KUMA KARANTA:Ƙungiyar NLC ta gudanar da zanga-zanga, saboda tsadar rayuwa a faɗin Najeriya

Amma wata ma’aikaciya da ta nemi a sakaya sunanta, ta ce wannan ba abu ne mai yiwuwa ba, domin ko albashin dubu sha takwas da gwamnatin baya ta ce a biya ma’aikata har yanzu wasu jihohi ba su biya ba, balle kuma ƙarin dubu talatin da gwamnatin baya ta yi. In an ce a ɗaga zuwa dubu ɗari shida har da goma sha biyar, wa zai iya biya? Wannan yaudara ce kawai.

Yusha’u Aliyu ƙwararre a fannin tattalin arziƙi, ya ce ba lallai ba ne gwamnati ta amince da wannan buƙata, domin za ta auna yawan ma’aikata da ta ke da su da kuma yawan kuɗin shiga da ta ke samu kafin ta amince. Saboda haka abu ne da zai zama sai an duba da idanun basira, domin a yanzu haka gwamnatin tana da basussuka da dama a kanta.

Ya zuwa yau dai ana bin gwamnatin Najeriya bashin akalla Naira Triliyan 87.9, kuma tuni har ofishin ƙididdiga ya fito da ƙiyasin cewa yawan hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya ya ƙaru zuwa kashi 33.20 a watan Maris ɗin 2024 daga kashi 31.70 cikin 100 a watan Fabrairun 2024.

Continue Reading

Labarai

Ƙungiyoyin ƙwadago sun sanar da janye yajin aikinsu

Published

on

Gamayyar ƙungiyoyin ƙwadago a Najeriya na NLC da TUC sun sanar da janye yajin aikin da suka fara ranar Talata.

Ƙungiyoyin de sun tsunduma yajin aikin sai-baba-ta-gani ne ranar Talatar domin nuna ɓacin ransu da dukan da aka yi wa shugaban NLC na ƙasa, Joe Ajaero a jihar Imo a kwanakin baya.

A lokacin dai Ajaero ya jagoranci ma’aikatan Imo domin wata zanga-zangar nuna rashin jin daɗi kan wasu manufofin gwamnan jihar, Hope Uzodinma.

Sai dai daga bisani wasu ’yan daba da ake zargin magoya bayan Gwamnan ne suka lakaɗa masa duka sannan ’yan sanda suka tsare shi.

Hakan dai ya janyo fushin ƙungiyoyin ƙwadagon, waɗanda suka tsunduma yajin aiki a ranar talata don nuna goyon bayansu gare shi.

KU KUMA KARANTA: Ba don kishin ƙasa ‘yan ƙwadago suka tsunduma yajin aiki ba – Gwamnati

Aminiya ya rawaito cewa Mashawarcin Shugaban ƙasa kan Harkokin Tsaro, Malam Nuhu Ribadu ya sa labule da ƙungiyoyin a ranar Laraba, a kan yajin aikin, inda ya ce tuni ma aka kama mutum biyu da ake zargi da duka Ajaeron.

Wakilinmu ya jiyo daga wasu jiga-jigan ’yan ƙwadago yayin taronsu na musamman suna cewa sun amince da ɗaukar matakin ne bayan nazarin dukkan alkawuran da Ribadun ya yi musu.

Shi ma Sakataren ƙungiyar ma’aikatan gwamnati ta AUPCTRE), Kwamared Sikiru Waheed, shi ma ya tabbatar da labarin ga ’yan jarida.

Continue Reading

'Yansanda

Hukumar ‘yan Sanda sun gargaɗi NLC kan zanga-zangar da suka shirya yi

Published

on

Muƙaddashin babban sufeton ‘yan sandan Najeriya, IGP Kayode Adeolu Egbetokun ya bayyana damuwa kan zanga-zangar da ƙungiyoyin ƙwadago suka shirya yi, inda ya yi gargaɗin cewa ‘yan sanda ba za su lamunci duk wani abu da zai kawo rikici ba.

KU KUMA KARANTA: Jirgin sama mai sauƙar ungulu ya faɗo a Legas

Sanarwar da kakakin rundunar ‘yan sandan Najeriya, ACP Olumuyiwa Adejobi ya fitar ta ce ‘yan ƙasa suna da ‘yancin yin zanga-zanga kamar yadda kundin mulki ya yi tanadi amma dole ne a gudanar da ita cikin kwanciyar hankali.

Rundunar ‘yan sandan ta ce a baya irin wannan zanga-zanga tana rikiɗewa ta zama tashin hankali, saboda haka ta ke gargaɗin cewa ba za ta bari a gudanar da duk wani abu da zai kawo matsalar tsaro ba.
ACP Adejobi ya ce duk wani yunƙurin tayar da rikici a lokacin zanga-zangar ƙungiyar ƙwadago zai fuskanci fushin hukuma.

Ƙungiyoyin ƙwadago a Najeriya sun shirya fara zanga-zanga a faɗin ƙasar daga ranar Laraba 2 ga watan Agusta domin nuna rashin amincewa da soke tallafin mai da gwamnati ta yi.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like