Ƙawayen amarya shida da ƙanin ango ɗaya, sun mutu a hatsarin mota a Neja

Daga Ibraheem El-Tafseer

Mutane 13 ne suka mutu a wani hatsarin mota da ya rutsa da su a kan titin Bida zuwa Mokwa a jihar Neja da ke arewacin Najeriya.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa mutum shida daga ciki mata ne da ke kan hanyarsu ta kai ƙawarsu amarya da ta yi aure.

Rahoton ya ce take suka mutu bayan faruwar haɗarin.

Ƙanin ango na cikin waɗanda suka rasa rayukansu.

Waɗanda suka shaida faruwar lamarin sun ce lamarin ya faru ne tsakanin ƙauyen Lukoro da Wuya a kan titin Bida zuwa Mokwa a yammacin Juma’a.

KU KUMA KARANTA: Mummunan hatsarin Mota ya ci rayukan mutane 18 a hanyar Kano zuwa Kaduna

Kwamandan hukumar kare hatsari ta Najeriya a Neja, Kumar Tsukwam wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ya ce mutane 13 ne suka mutu.

Ya ce haɗarin ya faru ne “tsakanin wata Toyota Corolla da Nissan ta haya da suka yi gaba da gaba, kuma mutum 13 sun mutu,” in ji Tsukwam.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *