Connect with us

Labarai

Ƙasurgumin ɗan ta’addan da ya addabi mutane a arewa, ya miƙa wuya ga sojojin Najeriya

Published

on

Rundunar sojojin Najeriya ta bayyana cewa wani ƙasurgumin kwamandan ƙungiyar ta’addanci na Boko Haram, mai suna Bulama Bukar, ya miƙa wuya ga dakarunta a yankin Gubio, jihar Borno.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da darakta labarai na rundunar soji, Birgediya Janar Onyema Nwachukwu, ya saki a ranar Laraba, 18 ga watan Oktoba, a Abuja.

Jaridar Daily Nigerian ta rawaito cewa ɗan ta’addan da ya miƙa wuya ya kasance kwamandan sansanin Boko Haram a Tapkin Chad da ke ƙauyen Gilima a ƙaramar hukumar Abadam ta jihar Borno.

Ya ƙara da cewar, kayayyakin da aka samo daga ɗan ta’addan da ya miƙa wuya sun haɗa da bindigar AK 47 guda ɗaya, makamai 5, harsasai 7.62 guda 44, wuƙa ɗaya, babur ɗaya da kuɗi Naira 23,500.

“A yanzu haka, ana ɗaukar bayanan ɗan ta’addan.”

A halin da ake ciki, kakakin rundunar sojin ya ce dakarun soji na nan suna aikin buɗe wuta domin raba ƙasar da tsagerun ‘yan ta’adda, masu tayar da ƙayar baya da sauran miyagu a faɗin ƙasar.

KU KUMA KARANTA: Rashin tsugunar da ‘yan Boko Haram da suka miƙa wuya babban haɗari ne- Barista Bulama Bukarti

Mista Nwachukwu ya ce a kan haka ne dakarun bataliya ta 2 suka kai kwantan ɓauna kan wasu ‘yan ta’adda a yankin Udawa dake ƙaramar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna a ranar 17 ga watan Oktoba sannan suka sheƙe ‘yan ta’adda uku.

Ya ce wutan da aka buɗe masu ya sa sauran sun tsere, yayin da sojojin suka ƙwato wata bindiga ɗauke da harsashi 111, babura biyu, babban rediyon sadarwa mai ƙarfin gaske da kuma wayoyi guda biyu.

A cewarsa, wani soja ya rasa ransa a yayin arangamar, rahoton Leadership.

Ya ƙara da cewar a wannan ranar, dakarun Birgediya ta 1 sun kama wani da ake zargin yana kai alburusai a ƙaramar hukumar Birnin Magaji da ke jihar Zamfara.

Ya ce binciken farko da aka yi ya nuna cewa wanda ake zargin yana hanyar kai wa wani shugaban ‘yan bindiga mai suna Gishiri harsashi ne.

A cewarsa, dakarun ‘yan banga sun ƙwato wata jaka ɗauke da harsashin 7.62mm guda 224, wayar hannu ɗaya da kuma kuɗi naira 4,000 daga hannunsa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like