No menu items!

Sample Page Title

Date:

Duk da takunkumin da Isra’ila ta saka, dubban Falasɗinawa daga yankin Yammacin Gabar Kogin Jordan da ta mamaye sun samu damar shiga Masallacin Ƙudus da ke Gabashin Birnin Ƙudus a ranar Juma’a ta farko ta watan Ramadan, don gabatar da sallarsu ta mako-mako a cikin jam’i yayin da suke azumi.

“Musulmai kusan 80,000 ne suka yi Sallar Juma’a a Masallacin Ƙudus,” in ji Ma’aikatar Kula da Harkokin Musulunci a Birnin Ƙudus a cikin wata sanarwa.

Sheikh Ekrima Sabri, babban limamin Masallacin Ƙudus, ya yaba wa Falasɗinawa muminai kan shiga masallacin duk da takunkuman Isra’ila.

KU KUMA KARANTA: Saudiyya ta jaddada cewa ba za ta shirya da Isra’ila ba, sai ta tsagaita wuta a Gaza

“Kwarararku mai albarka tana isar da saƙo ga masu kwaɗayin shiga masallacin cewa ba ruwansa da rarrabuwar kawuna kuma na Musulmai ne kawai, babu inda za a yi sulhu ko a bar wani ɓangare nasa,” ya shaida wa masallatan.

Sabri ya buƙaci al’ummar Musulmi da su zo Masallacin Ƙudus, yana mai cewa, “Idan aka hana su, za su iya yin salla a inda ta riske su, tare da fatan samun ladan yin salla a Masallacin Ƙudus.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...