Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya ta ayyana za’a shiga yajin aiki a watan Agusta a faɗin ƙasar

3
271

Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya (NLC) ta bai wa gwamnatin tarayya wa’adin kwanaki bakwai da ta janye duk wasu manufofin da ake ganin na yaƙi da talakawa ko kuma ta fuskanci yajin aikin gama gari daga ranar 2 ga watan Agusta.

Waɗannan manufofin sun haɗa da ƙarin farashin man fetur na kwanan nan.

Hakan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ƙungiyar NLC ta umurci dukkanin ƙungiyoyin ta da majalisun jihohin ƙasar nan da su gaggauta fara shirin ɗaukar ma’aikata da sauran ‘yan Najeriya da suka haɗa da ƙungiyoyin farar hula don gudanar da yajin aiki mai ɗorewa da kuma zanga-zangar gama gari idan gwamnati ta gaza biyan buƙatunta.

3 COMMENTS

Leave a Reply