No menu items!

Sample Page Title

Date:

Biyo bayan ƙarancin ruwan sama a Daminar bana ta 2023, Shehun Borno, Alhaji Abubakar Ibn Umar Garbai Elkanemi, ya ayyana taron addu’a domin neman taimakon Allah kan ruwan sama.

Don haka Shehu ya buƙaci al’ummar Musulmi da su fito gangamin taron jama’a domin halartar sallar jam’i da za a yi a nan gaba domin neman taimakon Allah domin samun ruwan sama a jihar.

Wata sanarwa da sakataren Shehun, Zannah Umar Ali ya raba wa manema labarai jiya a Maiduguri, ya ce za a gudanar da sallar raka’a biyu na neman ruwan sama a ranar Litinin a dandalin Ramat da ke Maiduguri da misalin ƙarfe 10:00 na safe.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin tarayya za ta magance ambaliyar ruwa a Jigawa – Shettima

Sanarwar ta buƙaci al’ummar Musulmi ba tare da la’akari da shekaru, jinsi da matsayi ba da su fito lungu da saƙo domin halartar addu’a don neman rahamar Allah a kan ƙarancin ruwan sama da ake fama da shi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...