No menu items!

Sample Page Title

Date:

Yan sanda a jihar Nasarawa na binciken bidiyon wata budurwa da ake zargin wani malamin jami’a ya ci zarafinta bisa zargin tana yunƙurin ƙwace wa ‘yar sa saurayi.

A bidiyon wanda ya karaɗe kafafan sada zumunta an nuno yadda aka ci zarafin budurwar mai shekaru 20 mai suna Blessing Mathias inda ake bugunta aka kuma kekece rigar jikinta da almakashi.

Cikin bidiyon an hasko malamin jami’ar da ke tsangayar koyar da ilimin tarihi na jami’ar tarayya ta garin Lafiya tare da wasu mutane suna cin zarafin Blessing.

Rahotanni sun ce Blessing ta yi yunƙurin ƙwace saurayin ‘yar malamin jami’ar ne bayan da ta faki idonta, ta ɗauki lambarsa a wayarta, lamarin da bai zo wa malamin jami’ar da makusantansa da da daɗiba har ta kai ga sun ɗauki matakin cin zarafinta.

Da yake martani akan bidiyon a kafar tweeter a ranar Asabar, mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan Legas Benjamin Hundai ya shaida cewa rundunar’yan sandan jihar Nasarawa na bincike akan lamarin.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...