Sheikh Saleh Al-Humaid ne zai jagoranci huɗubar Arfa na bana
Daga Jameel Lawan Yakasai
Masarautar Saudiya ta sanar da nadin Sheikh Saleh bin Abdullah Humaid a matsayin limamin da zai jagoranci Hudubar Arfa ta bana, tare da jagorantar sallah a masallacin Al Namirah, a ranar 9 ga Zul Hijjah.
KU KUMA KARANTA: Saudiyya ta hana Sheikh Gumi shiga ƙasar domin aikin Hajji
Sheikh Saleh Al Humaid mai shekaru 76, shi ne babban limamin masallacin Haramin Makkah, kuma ya shafe shekaru 43 yana limanci a masallacin.